Jami'an tsaron Masar sun kame masu zanga-zangar adawa da al-Sisi
Jami’an tsaron Masar sun kame mutane da dama, da suka shiga wata zanga-zangar adawa da shugaban kasar Abdel Fattah Al Sisi a jiya Juma’a.
Wallafawa ranar:
An dai soma zanga-zangar ce a filin Tahrir, inda ya zama cibiyar juyin juya halin da ya kawo karshen mulkin shugaba Hosni Mubarak.
Wani da ya shaida yadda abin ya faru, ya ce ba a jima da soma zanga-zangar ba ‘yan sandan dake cikin damara da taimakon masu farin kaya suka damke gungun masu zanga-zangar.
Tun a shekarar 2013 gwamnatin soji ta shugaba Al Sisi da ta kawar da shugabancin marigayi Muhd Morsi, ta haramta irin wannan zanga-zanga ta kin gwamnati.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu