Isa ga babban shafi

MSF ta zargi WHO da takaita raba magungunan Ebola a Congo

Kungiyar Agaji ta ‘Doctors Without Borders’ ta zargi Hukumar Lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya da takaita rarraba maganin cutar ebola a Jamhuriyar Dimokiradiyar Congo inda mutane sama da 2,100 suka mutu yanzu haka.

Health workers dressed in protective suits are seen at the newly constructed MSF(Doctors Without Borders) Ebola treatment centre in Goma, Democratic Republic of Congo, August 4, 2019.REUTERS/Baz Ratner
Health workers dressed in protective suits are seen at the newly constructed MSF(Doctors Without Borders) Ebola treatment centre in Goma, Democratic Republic of Congo, August 4, 2019.REUTERS/Baz Ratner REUTERS/Baz Ratner
Talla

Sanarwar da kungiyar ta fitar ta ce daya daga cikin matsalolin da su ke fuskanta wajen yaki da cutar ita ce karancin magani, abinda ya sa ake takaita rarraba shi ga tarin mabukata.

Kungiyar ta ce akalla mutane dubu 225 sun karbi allurar rigakafin cutar da kamfanin Merck na kasar Jamus ya samar, amma kuma duk da haka rigakafin ya yi karanci.

Kungiyar ta ce yunkurin ta na samar da maganin wajen hadin gwuiwa da ma’aikatar lafiyar Congo yaci tura, saboda yadda hukumar lafiya ta mamaye aikin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.