Afrika
'Yan bindiga sun kashe mutane a Burkina Faso
Hukumomin Burkina Faso sun ce akalla mutane 9 aka kashe lokacin da yan bindiga suka kai wasu hare hare guda biyu a yankunan dake fama da tashin hankali.
Wallafawa ranar:
Talla
Sanarwar tace an kai harin farko ne ranar asabar a Pissele dake kusa da Bourzanga, inda aka kashe mutane 6, yayin da aka kai hari na biyu a kauyen Bool-Kiiba inda aka kashe mutane 3.
Burkina Faso ta fada cikin tashe tashen hankula tun bayan kawar da shugaba Blaise Compaore daga karaga mulkin kasar, inda aka kashe mutane sama da 580 daga shekarar 2015 zuwa yanzu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu