Ko muhawara ta kasa za ta kawo karshen rikicin Kamaru?
Kasar Kamaru ta bude zaman muhawara ta kasa a wannan Litinin da zummar kawo karshen rikicin ‘yan aware da ke yankin masu magana da Turancin Ingilishi duk da cewa, jagororin ‘yan tawayen kasar sun ki shiga wannan muhawara.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Za a ci gaba da gudanar da muhawarar karkashin jagorancin Firaminista, Joseph Dion Ngute har zuwa ranar 4 ga watan Oktoba a wani babban dakin taro da ke birnin Yaounde.
Shugaba Paul Biya da ya shafe shekaru 37 kan karagar mulki, na fatan wannan muhawara za ta kawo karshen rikicin da ya haifar da tarnaki ga tattalin arziki kasar mai noman Kofi da Koko.
Sai dai gabanin fara wannan muhawara, da dama daga cikin masu rajin kare hakkin bil’adama da masharhanta sun bayyana shakkunsu, inda suke ganin taron ba zai yi tasiri ba.
Kusan mutane dubu 3 ne suka rasa rayukansu, yayin da rabin miliyan suka kaurace wa gidajensu tun bayan barkewar rikicin a shekarar 2017 tsakanin jami’an sojoji da ‘yan tawayen kasar da ke rajin ballewa daga Kamaru domin cin gashin kansu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu