Isa ga babban shafi
Duniya

Firaministan Habasha Abiy Ahmed ya lashe kyautar Nobel

A yau juma'a,kwamitin da ke da nauyin tantance mutanen da suka dace su lashe kyautar Nobel sun bayyana Firaministan Habasha Abiy Ahmed a matsayin wanda ya lashe kyautar Nobel ta zaman lafiya. 

Firaministan Habasha Abiy Ahmed
Firaministan Habasha Abiy Ahmed AFP/Monirul BHUIYAN
Talla

Firaministan Habasha na daya daga cikin mutanen da suka taka gaggarumar rawa wajen sulhunta kasar sa Habasha da Erythrea.

Kasashen sun koma aminan juna ne ranar 9 ga watan yuli bayan share kusan shekaru 20 suna kai ruwa rana.

A kasar Saudiya ne Firaministan Habasha da Shugaban kasar Erythrea suka rattaba hannu a takardar zaman lafiya tsakanin kasashen biyu.

Abiy Ahmed mai shekaru 43 dan kabilar Oromo ya samu mukamin Firaministan kasar ne a watan afrilun shekarar 2018.

Da samun wannan labari,Firaministan kasar Habasha ya nuna farin cikin sa tareda bayyana kyautar a matsayin kyauta zuwa nayihar Afrika

A cikin shekarar nan Gwamnatin kasar Habasha ta sanar da kashe mutumin da ake zargi da kitsa yunkurin juyin mulkin da bai yi nasara ba, a Yankin Amhara, bayan kashe babban hafsan sojin kasar da kuma shugaban Yankin.

Ofishin Firaminista Abiy Ahmed ya bayyana mutumin a matsayin Asaminew Tsige wanda aka taba daurewa da irin wannan yunkuri kafin Firaminista Ahmed ya sake shi a karkashin shirin sa na yiwa jama’a afuwa.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.