Firaministan Mali ya jagoranci bikin karbe makamai daga hannun yan tawaye
Firaministan Mali Boubou Cisse a jiya juma’a yayinda yake ziyara garin Mopti ya jagoranci bikin soma mika makamai daga hannun mayaka dubu 8500 a tsakiyar kasar.
Wallafawa ranar:
Yunkurin Firaministan kasar na zuwa ne a wani lokaci da kasar ta Mali ke fuskantar hare-hare daga mayankan jihadi.
Wata majiyar tsaro ta tseguntawa kamfanin dilancin labaren Faransa cewa akala mayaka 200 ne yanzu haka suka mika makaman suzuwa hukumomin a garin Mopti.
Shugaban hukumar dake da nauyin tattara wadanan makamai Zahabi Ould Sidy Mohamed yace akala mutane dubu 8.504 ne hukumar ta yi rijistan su ake kuma sa ran za su muka makaman su nan gaba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu