Mahara sun halaka masallata 16 a Burkina Faso
Akalla mutane 16 suka halaka wasu 2 suka jikkata a wani farmaki da mayaka masu ikirarin jihadi suka kai kan wani Masallaci a arewacin kasar Burkina Faso.
Wallafawa ranar:
Hukumomin tsaro a kasar sun ce, maharan sun afkawa masu ibadar ne a babban masallacin garin Salmossi misalin karfe 7 zuwa 8 na daren jiya Juma’a, inda suka bude musu wuta.
Duk da cewa Burkina Faso na daga cikin kasashen Afrika masu fama da hare-haren ta’addanci, mafi akasarin ‘yan kasar na adawa da kasancewar sojojin kasashen ketare a kasar, musamman na Faransa da ta yi musu mulkin mallaka.
A ranar asabar da ta gabata, kimanin mutane dubu 1 suka yi zanga-zanga a Ouagadougou, babban birnin kasar, don yin Allah-wadai da ta’addanci da kuma kafa sansanonin sojojin kasashen Turai da Amurka a nahiyar Afrika.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu