Isa ga babban shafi
Mali

'Yan bindiga sun sace malaman makaranta

Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton cewar masu ikirarin jihadi ne, sun sace malamai 6 a yankin tsakiya Mali, saboda yin magana da kuma koyar da dalibai cikin harshen Faransanci.

Wasu sojojin kasar Mali.
Wasu sojojin kasar Mali. AFP/PHILIPPE DESMAZES
Talla

Wani shaidar gani da ido, ya ce kafin sace malaman, sai da ‘yan bindigar suka kona tarin litattafan dalibai a farfajiyar makarantar.

Harin na baya bayan nan ya zo ne bayan da wata kididdiga ta nuna cewar, sama da makarantu 900 aka rufe a sassan kasar Mali, sama da kashi 2 bisa 3 daga cikinsu kuma a yankin tsakiyar kasar, saboda matsalolin tsaron da suka hada da na ta’addanci da kuma rikicin kabilanci.

A shekarar 2012 matsalar tsaro ta girmama a Mali, bayan da mayakan masu ikirarin jihadi da suka yi wa kungiyar Al-Qaeda mubaya’a suka mamaye arewacin kasar, bayan da sojojin kasar suka gaza murkushe tawayen Azbinawa.

Sai dai a shekarar 2013 dakarun Faransa suka kawo dauki, inda suka yi nasarar kwace mafi akasarin yankunan da mayakan suka mamaye.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.