Isa ga babban shafi
Mali-Sahel

Shekaru 6 da kashe Ghislain Dupont da Claude Verlon a Mali

Ranar 2 ga watan nuwambar shekara ta 2013 ne ‘yan bindiga suka hallaka Ghislaine Dupont da kuma Claude Verlon, dukanninsu ma’aikatan RFI, bayan sace su a wani wuri da ke kusa da birnin Kidal na arewacin kasar Mali.

Ma'aikatan RFI, Claude Verlon (Hagu) da Ghislaine Dupont (Dama) wadanda aka yi wa kisan gilla a Mali a 2013.
Ma'aikatan RFI, Claude Verlon (Hagu) da Ghislaine Dupont (Dama) wadanda aka yi wa kisan gilla a Mali a 2013. RFI
Talla

Shekaru 6 bayan faruwar wannan lamari, har yanzu masu bincike ba su gano dalilan yin garkuwa da wadannan mutane balantana kisan da aka yi masu ba, kuma har zuwa yau, ba daya daga cikin mutanen da suka aikata wannan danyen aiki da aka kama ko hukuntar da shi.

A wancan lokaci dai kungiyar al-Qaida a yankin Magreb, ta fito fili inda ta dauki alhakin kashe mutanen biyu.

Duk da cewa binciken da ake gudanarwa dangane wannan lamari na fuskantar tafiyar hawainiya, to amma majiyoyi a kusa da masu binciken sun ce ana samu ci gaba daidai gwargwado.

Lambobin wayoyin da masu bincike suka samu a cikin motar da maharan suka kaurace wa bayan sun kashe Dupond da Verlon, sun bayar da damar samun karin haske a game da wasu mutane 12 da suka yi musayar wayoyi da maharan.

Ma’ikatar shari’a Faransa, na ci gaba da fadada bincike, inda tuni alkali ya bukaci kamfanonin waya na Orange Mali da Malitel a kasar Mali su ba da hadin-kai a wannan bincike, to sai dai ba a samu irin goyon bayan da ake bukata daga kamfanin Malitel ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.