Isa ga babban shafi
Afrika

Wani gini ya rufta a Lagos

A marecen jiya asabar wani gini ya rufta aunguwar Ikoyi dake jihar Lagos. Shugaban hukumar kula da agajin gaggawa a jihar Lagos da ke tarayyar Najeriya, Olufemi Oke-Osanyintolu ya tabbatar da cewa an ceto mutane 4 daga karkashin wanan gini da ya rufta a marecen jiya.

Masu aikin ceto bayan rugujewar ginin
Masu aikin ceto bayan rugujewar ginin ANDREA LEONI / AFP
Talla

Ginin da ya rufta, daya ne daga cikin benaye guda hudu da ake kan ginawa a Clover Court, kuma ya rufta ne a hawa na biyu daidai lokacin da ake zuba kankare. Wasu majiyoyi sun ce daya daga cikin lebarorin da ke aiki a wurin ya rasu, yayin da sauran suka samu raunuka.

Rugujewar gine-gine masu tsayi dai ba sabon abu ba ne a Najeriya don ko a watan Satumban 2014 ma akalla mutane 116 ne suka mtu bayan fadowar wani gini mai hawa 6 a jihar Lagos ciki har da 'yan kasar Afrika ta kudu 84, wanda daga bisani kuma aka gano cewa an yi ginin ne ba bisa ka'ida ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.