Isa ga babban shafi
Mali-Ta'addanci

Maharba sun sake farmakar Fulani a Mali

Majalisar Dinkin Duniya ta koka da yadda hare-hare kan kauyuka a Mali ke ci gaba da ta’azzara dai dai lokacin da harin daren Alhamis din nan kan kauyukan Fulani ya hallaka mutane 14 tare da jikkata wasu mutum 2.

Dakarun Soji a kauyen Mali.
Dakarun Soji a kauyen Mali. RFI/Coralie Pierret
Talla

Adadin na Majalisar Dinkin Duniya kan mutane da suka mutu a harin dai ya banbanta da adadin da jami’an tsaron kasar suka bayar da ya nuna mutane 15 suka kwanta dama a harin kabilancin.

A cewar ma’aikatar tsaron Mali dai, wasu mahaya ne kan babaura sanye da shiga irinta Maharba da aka fi sani da Dozo suka farmaki kauyen Siba tare da hallaka Fulanin.

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa baya ga mutanen 15 da suka mutu maza 5 mace guda, maharani sun kuma kone kauyen kurmus.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.