Isa ga babban shafi

An kammala yakin neman zaben shugaban kasa a Togo

A ranar Alhamis za a kawo karshen yakin neman zaben shugaban kasa wanda za a yi ranar Asabar mai zuwa a Togo.

Hukumar zaben kasar Togo ta sanar da shirin gudanar da zaben shugaban kasar ranar Asabar mai zuwa
Hukumar zaben kasar Togo ta sanar da shirin gudanar da zaben shugaban kasar ranar Asabar mai zuwa PIUS UTOMI EKPEI / AFP
Talla

Shugaban hukumar zaben kasar Tchambakou Ayassor, ya ce tuni hukumarsa ta dauki matakan da suka dace don tabbatar da cewa an isar da kayan aiki a rumfunan zabe dubu 9 da 300 a sassan kasar.

Mutane 7 ne ciki har da shugaba mai ci Faure Gnasingbe za su tsaya a takara a zaben na ranar Asabar.

'Yan  adawa na ci gaba da bayyana damuwa kan takarar neman wa'adi na 4 da Shugaban kasar Faure Gnasingbe da ya gaji mahaifinsa wanda ya yiwa kasar rikon kama karya tareda murkushe duk wani bore daga bangaren yan adawa ya yi.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.