Isa ga babban shafi
Nepal

Mutane da dama sun mutu a wata girgizan kasa a Nepal

Mutane kusan 30 aka ruwaito sun mutu a wata girgizan kasa mai karfin maki 7.3 da ta sake shafar yankin gabacin kasar Nepal kusa da tsaunin Everest bayan sama da mutane 8,000 sun mutu a mummunar girgizan kasa da ta abkawa Nepal  makwanni biyu da suka gabata.

masu aikin ceto a kasar Nepal
masu aikin ceto a kasar Nepal AFP PHOTO / PRAKASH MATHEMA
Talla

Mahukuntan kasar sun ce adadin mutane kusan 30 suka mutu yayin da sama da 1000 suka samu rauni sakamakon girgizan kasar da ta shafi gabacin kasar.

Masu aiko da rahotanni sun ce Girgizan kasar ta auku ne da musalin karfe 12:35 na rana a gabacin Kathmandu babban birnin kasar bayan girgizan kasa mai karfi maki 7.8 ta yi mummunan ta’adi a yammacin Nepal makwanni biyu da suka gabata.

 

Girigizan kasar ta shafi yankin India  tare da rusa gidaje a yankin kabilar Tibet a China.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.