Isa ga babban shafi
china

An ceto mutane 4 bayan kwanaki 36 a karkashin kasa a China

An yi nasarar ceto wasu mutane hudu mahaka ma’adinai a kasar China bayan sun shafe kwanaki 36 makale a karkashin a kasa, al-amarin da aka bayyana a matsayin abin al-ajabi. 

Tun a watan Disamban bara kasa ta rubta da mahaka ma'adinan karkashin kasar guda 29 amma har yanzu ba a ji duriyar mutane 13 ba.
Tun a watan Disamban bara kasa ta rubta da mahaka ma'adinan karkashin kasar guda 29 amma har yanzu ba a ji duriyar mutane 13 ba. cnn.com
Talla

An shafe sa’oi biyu ana aikin ceto mutanen daga karkashin kasa mai zurfin sama da mita 200 kamar yadda kafar talabijin ta CCTV a China ta rawaito.

Mutanen dai na cikin mahaka ma'adinai  29 da kasa ta rubta da su a ranar 25 ga watan Disamabn bara, to sai dai ba a gamsu da aikin ceton ba, lura da cewa akwai sauran mutane 13 da har yanzu ba a ji duriyarsu ba kuma a jumulce mutane 15 kenan aka ceto  yayin da aka tabbatar da mutuwar mutun guda.

An dai kwatanta aukuwar lamarin da irin wanda ya faru a shekara ta 2010 a kasar Chile, inda aka ceto mutane 33 bayan suma sun shafe kwanaki 69 makale a karkashin kasa.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.