Afghanistan
Taliban ta kai sabon hari a Tarin kot
Kungiyar Taliban ta kai hari kan jami’an tsaron da ke garin Tarin Kot a kasar Afghanistan a yunkurin da ta ke na kama wasu garuruwan kasar.
Wallafawa ranar:
Talla
Wani shugaban kabilar da ke garin Haji Baridad ya ce mayakan kungiyar sun kauda daukacin wuraren da jami’an tsaro suka sanya shinge kafin shiga garin.
Sai dai mai Magana da yawun gwamnan Yankin Mohammed Nayab ya ce ba za su bar maharani su samu nasara ba.
Wannan shine hari na uku a garuruwa dabam dabam da kungiyar ke kaiwa a cikin 'yan makwannin nan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu