Isa ga babban shafi
Turkiya

Hukuncin daurin rai da rai kan masu hannu a yunkurin juyin mulki

Masu shigar da kara a Turkiya sun bukaci hukuncin dauri na iyakacin rayuwa kan mutane akalla 50 da ake zargi da yunkurin juyin mulkin da bai yi nasara ba a watan Yulin  da ya gabata.

Shugaba Recep Erdoghan ya sha alwashin hukunta masu hannu a yunkurin yi masa juyin mulki.
Shugaba Recep Erdoghan ya sha alwashin hukunta masu hannu a yunkurin yi masa juyin mulki. REUTERS/Osman Orsal
Talla

Ana zargin mutanen ne da hadin baki domin kashe shugaba Recep Tayip Erdogan a wani wurin hutawa inda shugaban ya ke tare da iyalansa a lokacin.

Daga wannan wurin shakatawa ne dai Shugaban ya bar wajen ba shiri zuwa birnin Santanbul inda ya ke cewa ya bar wurin ana saura mintoci 15 a kashe shi.

Tun bayan wannan yunkurin juyin mulkin shugaba Erdoghan ya sa ana tsare mutane fiye da dubu uku a gidan yarin kasar baya ga wasu da dama da aka sallama daga aiki bisa zargin hannu a juyin mulkin.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.