Isa ga babban shafi
Iraq

Yaki a Mosul ya raba mutane rabin miliyan da gidajensu

Majalisar Dinkin Duniya tace watanni shida da aka kwashe ana fafatawa don neman karbe birnin Mosul daga hannun kungiyar mayakan ISIS ya raba mutane kusan rabin miliyan da gidajensu. 

Rabin Miliyan suka tserewa yaki a Mosul na Iraqi
Rabin Miliyan suka tserewa yaki a Mosul na Iraqi REUTERS
Talla

Lise Grande, jami’ar aikin jinkai na Majalisar a Iraqi ta ce adadin yan gudun hijirar da ke ci gaba da ficewa Mosul na dada karuwa.

Jami’ar ta ce, hasashen da suke da shi na mutanen da ke iya barin garin kafin fara yakin bai wuce miliyan guda ba, amma yanzu haka sama da 493,000 sun fice daga garin, ba tare da daukar komai ba, yayin da adadin ke ci gaba da karuwa.

Majalisar tace yanzu haka akwai mutane 500,000 da rikicin ya ritsa da su a yankin da mayakan ISIS ke rike da shi.

A wata ziyara da ya kai sansanonin mutanen da rikicin Mosul ya raba da gidajensu, Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya bayyana ayyukan jin kai na bukatar tallafi domin kula da yan gudun hijirar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.