Bakonmu a Yau
Sani Inuwa Adam: Ziyarar Trump a yankin gabas ta tsakiya
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:43
A Talatar nan shugaban kasar Amurka Donald Trump, ke kamala ziyarar da ya soma a yankin Gabas ta Tsakiya, wacce ta kai shi Saudiya, Isra’ila da kuma yankin Falasdinu. Baya ga batun tattalin azriki da Mista Trump ya tattauna kai da Hukumomin Saudiya, akwai batun tsaro a Isra’ila da kuma farfado da tattaunawar yiwuwar samar da yankin Falasdinu. Yayin zantawarsa da Aminu Sani Sado, Sani Inuwa Adam masani harkokin Gabas ta tsakiya ya ce da wuya ziyarar ta Trump tayi tasiri kan batun samar da zaman lafiya a gabas ta tsakiya.