Iraqi
Dan kunar bakin wake ya kashe mutane 27 a Iraqi
Hukumomin tsaron Iraqi sun bayyana cewa, wani dan kunar bakin wake ya kashe mutane 27 bayan ya tayar da bama-baman da ke makare a cikin motarsa a wani shagon cimaka a birnin Bagadaza.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Talla
Harin wanda aka kai a dai dai lokacin da jama’a ke bude bakin azumin Ramadan, ya kuma raunana mutane 30.
Kafar Amaq da kungiyar ISIS ke yada farfagantarta, ta rawaito cewa, an kai harin ne kan mabiya Shi’a a kasar.
Kungiyar ISIS dai na kallon mabiya Shi’a a matsayin ‘yan bidi’a , abin da ya sa ta ke yawan kaddamar mu su da hare-hare a kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu