Isa ga babban shafi
Iraqi

Dan kunar bakin wake ya kashe mutane 27 a Iraqi

Hukumomin tsaron Iraqi sun bayyana cewa, wani dan kunar bakin wake ya kashe mutane 27 bayan ya tayar da bama-baman da ke makare a cikin motarsa a wani shagon cimaka a birnin Bagadaza.

Kungiyar ISIS na yawaita kai hare-hare kan mabiya Shi'a masu rinjaye a Iraqi
Kungiyar ISIS na yawaita kai hare-hare kan mabiya Shi'a masu rinjaye a Iraqi REUTERS/Alaa Al-Marjani
Talla

Harin wanda aka kai a dai dai lokacin da jama’a ke bude bakin azumin Ramadan, ya kuma raunana mutane 30.

Kafar Amaq da kungiyar ISIS ke yada farfagantarta, ta rawaito cewa, an kai harin ne kan mabiya Shi’a a kasar.

Kungiyar ISIS dai na kallon mabiya Shi’a a matsayin ‘yan bidi’a , abin da ya sa ta ke yawan kaddamar mu su da hare-hare a kasar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.