Isa ga babban shafi
Iraqi

IS ta rusa masallacin da Baghadi ya kira kansa Kalifa

Magoya bayan kungiyar IS sun tarwatsa masallacin Al-Nuri da shugabansu Abubakar Al-Baghdadi ya gabatar da hudubarsa ta farko a matsayin Khalifa shekaru biyu da suka gabata a birnin Mosul.

Jagoran IS Bakr al-Baghdadi yana huduba a Masallacin Nuri a Mosul
Jagoran IS Bakr al-Baghdadi yana huduba a Masallacin Nuri a Mosul REUTERS/Social Media Website via Reuters TV
Talla

Laftanal Janar Abdul-Amir Yarallha babban kwamandan rundunar da ke kokarin kwace birnin Mosul, ya ce mayakan na Daesh sun tarwatsa masallacin ne a daidai lokacin da dakarun gwamnati suka doshi masallacin.

Masallacin na daga cikin masallatai mafi dadewa a birnin Mosul mai tarihi a cikin Iraqi.

Gwamnatin Iraqi ta danganta rusa masallacin a matsayin nasara akan Mayakan IS da aka shafe watanni takwas ana yakarsu domin kwato garin Mosul.

A watan Yunin 2014 ne IS ta ayyana kafa daula bayan kwace Mosul, kuma a lokacin ne aka nuna shugaban kungiyar Baghdadi a Masallacin yana huduba tare da bayyana kansa a matsayin Kalifa.

Sai dai kungiyar IS ta ce dakarun Iraqi ne suka rusa masallacin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.