Isa ga babban shafi
Saudiya-Yemen

Saudiya ta ce kuskure ne harin da ta kai wa fararen hula a Yemen

Rundunar sojin hadaka da Saudiyya ke jagoranta, ta dauki alhakin harin da jiragen yaki suka kai a birnin Sana’a wanda ya hallaka fararen hula 14 ciki harda kananan yara.

Wasu mutane da ke kokarin duba baraguzan ginin da jiragen yakin Saudiya suka kai wa farmaki a birnin Sanaa da ke Yemen Agusta 25, shekarar 2017.
Wasu mutane da ke kokarin duba baraguzan ginin da jiragen yakin Saudiya suka kai wa farmaki a birnin Sanaa da ke Yemen Agusta 25, shekarar 2017. REUTERS/Khaled Abdullah TPX IMAGES OF THE DAY
Talla

Sai dai kakakin rundunar hadakar Kanal Turki al-Malki, ya ce, an samu kkuskure ne na na’ura ba wai da niyya aka farwa fararen hular ba.

Al-Malki ya bayyana nadamar rundunar tare da yi wa iyalan wadanda harin ya ritsa da su ta’aziyya.

Kakakin ya kuma zargi mayakan Houthi mabiya mazhabar Shi’a da kafa bariki hadi da cibiyar yada sakwanni a kusa da gidajen fararen hula.

Tun a shekara ta 2014 yankin ke karkashin mayakan Houthi bayan korar sojin gwamnatin kasar ta Yemen da suka yi a waccan lokaci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.