Isa ga babban shafi
Falesdinu

Yarjejeniyar sulhu tsakanin Hamas da Fatah

Yarjejeniyar da bangarorin biyu suka cimma bayan Masar ta shiga tsakaninsu, ta kunshi cewa  kungiyar Fatah da ke da rinjaye a  hukumomin Falasdinu sannan kuma ke zaune a gabar Yammacin Kogin Jordan, za ta karbi ikon  tafiyar da   yankin Gaza nan da ranar 1 ga watan Disamba.

Tutar Hamas da Fatah na Palasdinu
Tutar Hamas da Fatah na Palasdinu REUTERS/Ibraheem Abu Mustafa
Talla

A shekarar 2007 ne aka fatattaki mahukumomin daga  Gaza, amma a cikin watan jiya ne Hamas ta amince ta mika ma ta mulkin fararen hular yankin.

A cewar yarjejeniyar, bangarori da dama da ke hammaya da juna a Falasdinu da suka hada da Hamas da Fatah, za su gana a ranar 21 ga watan Nuwamba mai zuwa a birnin Al-Kahira na Masar don tattauna kan samar da gwamnatin  hadaka.

Kazalika, za a  mika kan iyakar Gaza da Isra’ila da Masar ga hukumomin Falasdinu nan da makwanni masu zuwa.

Har ila yau, yarjejniyar ta ce, shugaban Falasdinu Mahmud Abbas zai ziyarci Gaza a karon farko cikin shekaru 10 nan da kwanaki kalilan.

Sannan  kuma nan da watan Fabairun 2018 ne, ake sa-ran warware matsalar dubban mutanen gwamnati da Hamas ta dauka aiki.

Kana, za a samar da sausauci dangane da tsauraran matakai da hukumomin Falasdinu suka dauka a Gaza, cikinsu har da batun kudin da mazauna yankin ke biya don samun makamashi.

Sai dai har yanzu, akwai sauran wasu batutuwa da bangarorin biyu ba su cimma matsaya a kansu ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.