Isa ga babban shafi
Myanmar

An tilastawa 'yan gudun hijira komawa Myanmar

Hukumomi a Bangaladesh sun bada sanarwar cewa akwai karin dubban Musulmi ‘yan kabilar Rohingya a kan iyakar kasar da Myanmar wadanda ke jiran samun damar tsallakowa kasar don samun mafaka, sakamakon kisan gillar da ake ci gaba da yi musu.

Wasu daga cikin musulmi 'yan kabilar Rohingya kenan bayan da kwale-kwalensu ya kife a kokarin da suke na tsallakawa Bangladesh don gujewa rikici a jihar Rakhine ta Myanmar.
Wasu daga cikin musulmi 'yan kabilar Rohingya kenan bayan da kwale-kwalensu ya kife a kokarin da suke na tsallakawa Bangladesh don gujewa rikici a jihar Rakhine ta Myanmar. Reuters/路透社
Talla

A cewar hukumomin sun rufe kan iyakokin kasar da 'yan gudun hijirar ke samun tsallakowa, sakamakon yawan da suke ci gaba da yi kowacce rana a kasar.

Ko a makon daya gabata ma, kimanin musulmi ‘yan kabilar Rohingya dubu 10 aka dakatar tsawon kwanaki uku a wani kauye na Anjumanpara kafin ba su izinin shigowa Bangaladesh a ranar Alhamis.

Galibin ‘yan gudun hijirar da ke neman tsallakowa Bangaladesh na kukan rashin abinci a kauyukansu bayan da hukumomi a Rakhine suka hana shigar musu da kayakin Abinci

Wani jami’in tsaro ya ce galibi masunta ne ke tsallako da ‘yan gudun hijirar ta ruwan da ya raba kasashen biyu, lamarin da ya sa aka dakatar da aikinsu na wucin gadi tare da mayar da ‘yan gudun hijira kimanin dubu 15 Myanmar kafin su samu damar tsallakowa ruwan.

Kawo yanzu dai adadin musulmi 'yan kabilar Rohingya da rikici ya tilastawa barin gidajensu ya haura mutum dubu dari shidda a Bnagaladeshi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.