MDD ta zargi Korewa ta Arewa da fasakaurin makamai
Jami’an sa ido na Majalisar Dinkin Duniya sun ce, Korea ta Arewa ta bijirewa takunkuman da Majalisar ta kakaba mata, na haramcin fitar da wasu kayayyaki zuwa ketare.
Wallafawa ranar:
Rahoton ya ce bijirewa takunkuman ya bai wa kasar damar samun kudaden shiga akalla dala miliyan 200 a shekarar 2017.
Jami’an sun ce Korea ta Arewa ta samu makudan kudaden shigar ne daga cinikayyar makamashin Kwal da ta fitar zuwa Rasha, China, Korea ta Kudu, Malaysia da kuma Vietnam, inda ta yi amfani da takardun da ke nuna kwal din ya fito ne daga kasashen Rasha da China.
Rahoton Majalisar Dinkin Duniyar, ya kuma zargi Korewa ta Arewa, da fasa kaurin makamai zuwa kasashen Syria da kuma Myanmar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu