Philippines
Kotun ICC ta kaddamar da bincike kan shirin shugaban kasar Philippines
Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa, ICC ta kaddamar da bincike kan shirin shugaban kasar Philippines Rodrigo Duterte na yaki da tu’ammuli da miyagun kwayoyi da ya kaddamar a watan Yuly na shekarar 2016, wanda cikinsa aka hallaka dubban ‘yan kasar.
Wallafawa ranar:
Talla
Babbar mai gabatar da kara a kotun ta ICC Fatou Bensouda, ta ce binciken zai mayar da hankali ne kan zargin Duterte da take hakkin dan adam.
Akalla ‘yan kasar Philippines dubu 4,000, ‘yan sandan kasar suka hallaka, bisa da’awar sun same su da laifin tu’ammuli da miyagun kwayoyi ko kuma safararsu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu