Isa ga babban shafi
Iran

Sabon rikici tsakanin Iran da Isra'ila

A yau asabar kasar Iran ta zargi Isra’ila da shirya makarkashiya da kage bayan da hukumar tsaron Isra’ila ta bayana kakabo wani jirgi marasa matuki na kasar Iran.

Hassan Rohani Shugaban kasar Iran
Hassan Rohani Shugaban kasar Iran Handout / Iranian Presidency / AFP
Talla

Mai magana da yahu ministan harakokin wajen Iran Bahram Ghassemi ya bayana Isra’ila a matsayin wacce ke kokarin yi rufa –rufa ga kisan da take aikatawa a yankunan Syria da gabas ta taskiya.

A matakin mayar da martani daga Syria bayan da Isara’ila ta aike da jiragen ta na yaki zuwa wasu yankunan kasar Syria, rundunar tsaron Syria ta yi nasarar kakabo daya daga cikin jiragen yakin Isra’ila wanda aka bayyana cewa matuki ya samu munanan raunuka.

Jami’in Diflomasiya na Iran ya karasa da cewa kasar sa ba ta aike da soji ba a Syria, sai dai ta na dafawa dakarun Syria da shawarwari da dabaru na yaki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.