Jiragen yakin Isra'ila sun sake kai farmaki cikin Syria
Fira ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya gargadi Iran da cewa, Isra’ila zata maida martani ta fuskar karfin soji, kan duk wata barazanar tsaro daga gareta.
Wallafawa ranar:
Gargadin na Isra’ila ya zo ne bayan kai farmaki na biyu da jiragen yakinta suka yi kan wasu cibiyoyin tsaro 12 a Syria wadanda ke karkashin Iran da kuma gwamnatin Syria.
Isra’ila ta ce ta kai farmakin ne bayan da ta kakkabo wani jirgin leken asiri na Iran da ke kokarn shiga cikin kasar daga Syria.
Netanyahu ya jaddada cewa Isra’ila zata kalubalanci duk wani yunkuri na Iran wajen kafa cibiyoyin sojinta a Syria, abinda ta ke kallo a matsayin babbar barazana gareta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu