Isa ga babban shafi

Jiragen yakin Isra'ila sun sake kai farmaki cikin Syria

Fira ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya gargadi Iran da cewa, Isra’ila zata maida martani ta fuskar karfin soji, kan duk wata barazanar tsaro daga gareta.

Wani sashi na arewacin kasar Syria, inda jirgin yakin Isra'ila ya fadi bayan harbo shi kasa da soji masu biyayya ga Iran da Syria, suka yi.
Wani sashi na arewacin kasar Syria, inda jirgin yakin Isra'ila ya fadi bayan harbo shi kasa da soji masu biyayya ga Iran da Syria, suka yi. AFP / Jack GUEZ
Talla

Gargadin na Isra’ila ya zo ne bayan kai farmaki na biyu da jiragen yakinta suka yi kan wasu cibiyoyin tsaro 12 a Syria wadanda ke karkashin Iran da kuma gwamnatin Syria.

Isra’ila ta ce ta kai farmakin ne bayan da ta kakkabo wani jirgin leken asiri na Iran da ke kokarn shiga cikin kasar daga Syria.

Netanyahu ya jaddada cewa Isra’ila zata kalubalanci duk wani yunkuri na Iran wajen kafa cibiyoyin sojinta a Syria, abinda ta ke kallo a matsayin babbar barazana gareta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.