Isa ga babban shafi

Kim Jong Un ya bukaci tattaunawa kai tsaye da Korea ta Kudu

Shugaban Korea ta Arewa Kim Jong Un, ya gayyaci takwaransa na Korea da Kudu Moon Jae-in don tattaunawa a babban birnin kasarsa, Pyongyang.

Shugaban Korea ta Kudu Moon Jae-in yayin tattaunawa da tawagar Korea ta Arewa, cikin har da kanwar shugaban Korea ta Arewa, Kim Yo Jong.
Shugaban Korea ta Kudu Moon Jae-in yayin tattaunawa da tawagar Korea ta Arewa, cikin har da kanwar shugaban Korea ta Arewa, Kim Yo Jong. Yonhap via REUTERS
Talla

Karo na farko kenan cikin sama da shekaru 10, da shugabannin kasashen biyu, zasu gana kai tsaye.

Kanwar shugaban Korea ta Arewa Kim Yo Jong ce ta mika sakon gayyatar tattaunawar da baki, a lokacin da tawagar Korea ta Arewan ta ke ganawa da shugaban Korea ta Kudu Moon Jae-in fadar gwamnatinsa.

A ranar Juma’a ne dai aka fara gasar Olympics ta hunturu a Korea ta Kudu, wadda ‘yan wasan korea ta Arewa ke halarta, duk da cewa ba’a ware-ware matsalar diflomasiya tsakanin bangarorin biyu ba, wadda ta smo asali a dalilin shirin Korea ta arewan na mallakar makaman nuukiliya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.