Isa ga babban shafi
Iran

Iran ta bukaci kasashen turai su lalata makaman nukiliyarsu

Kasar Iran ta ce, ba zata tattaunawa da kasashen turai da Amurka ba, kan shirinta na ci gaba da kera manyan makamai masu Linzami, sai dukkanin kasashen, sun lalata makaman nukiliyar da suka mallaka da sauran makamai masu linzami da ke cin dogon zango.

Wasu daga cikin sabbin makamai masu linzami da kasar Iran ta kera, masu cin dogon zango,  a filin raeo na  Baharestan da ke Teheran, baban birnin Iran.
Wasu daga cikin sabbin makamai masu linzami da kasar Iran ta kera, masu cin dogon zango, a filin raeo na Baharestan da ke Teheran, baban birnin Iran. Nazanin Tabatabaee Yazdi/TIMA REUTERS
Talla

Iran ta jaddada cewa munafar shirinta na kera manyan makamai masu linzami ya dogara ne akan samar wa da kanta tsaro daga duk wata barazana, kuma shirin kera makamai masu linzamin ba shi da alaka da yarjejeniyar nukiliyar da ta cimma da manyan kasashen duniya a 2015.

Iran ta amince da dakatar da shirinta na inganta makamashin nukilya wanda ta musanta cewa kokarin kera makami mai Linzami, sai dai Iran din taki amincewa da bukatar zama a tattauna da ita kan shirin ta kan mallakar karin manyan makamai masu linzami.

Tuni dai kasashen turai suka fara tattaunawa kan rawar da Iran ke takawa a yankin gabas ta tsakiya, kuma a cikin wannan wata na Maris zasu gudanar da makamancin taron akan Iran, a kasar Italiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.