Sakataren harkokin wajen Amurka na ziyara a Gabas ta Tsakiya
Sakataren harkokin wajen Amurka Mike Pompeo ya isa kasar Saudiyya, inda ya fara ziyarar kwanaki uku a yankin gabas ta tsakiya, wadda a cikinta zai ziyarci kasashen Jordan da Isra’ila.
Wallafawa ranar:
Ana sa ran ziyarar ta Mike Pompeo zata mayarda da hankali ne akan yarjejeniyar nukuliyar Iran, wadda shugaban Amurka Donald Trump ke fatan a yiwa garambawul.
A farkon shekarar da muke ciki ne kuma Trump ya yi barazanar janye amurka daga yarejejeniyar, muddin ba a sauya mata fasali ba, nan da zuwa 12 ga watan Mayu.
Kasashen da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar nukiliyar Iran a shekarar 2015, sun hada da Birtaniya, Faransa, Jamus, Rasha da kuma China.
Ra’ayin baki dayan kasashen ya ci karo da na Amurka da ke neman a sake fasalta yarjejeniyar, kudurin da itama kasar Iran da ci alwashin ba zata lamunci kyale aiwatar da shi ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu