Tawagar Majalisar dinkin Duniya ta ziyarci sansanin yan Rohingya
Daruruwan yan kabilar Rohingya ne suka gudanar da zanga zangar lumana lokacin da wakilan kwamitin Sulhu na Majalisar dinkin Duniya suka ziyarci sansanin su dake Bangladesh domin ganin halin da suke ciki.
Wallafawa ranar:
Bayanai sun ce wasu daga cikin yan gudun hijirar sun barke da kuka lokacin da suke yiwa jakadun bayani kan irin azabar da suka fuskanta daga hannun sojojin Myanmar wadanda suka dinga kashe su, suna yiwa matan su fyade.
Yanzu haka jakadun 15 dake kwamitin sulhu na ziyarar kwanaki 4, inda ake saran za su ziyarci Myanmar domin ganawa da jagorar gwamnati Aung San Suu Kyi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu