Faransa ta kwace kadarar wasu kamfanoni bisa alaka da makami mai guba
Ministan kudi na Faransa Bruno Le Maire, ya sa hannu kan takardar umarnin gwamnati na kwace ilahirin kadarorin wasu kamfanoni da ke kasar, tsawon watanni 6.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Faransa ta dauki matakin akan kamfanonin da hedikwatocinsu ke kasashen Syria, Lebanon da China, bayan bankado cewa suna da hannu wajen safara da kera makamai masu guba a Syria, da aka yi amfani da su wajen hallaka fararen hula a kasar.
A watan Janairu da ya gabata, Faransa ta hukunta wasu mutane 25 da kamfanoni da ke da hedikwata a Syria ta hanyar kwace musu kadarori da kakaba musu takunkumi, bisa zarginsu da taimakawa samar da makamai masu guba a kasar ta Syria.
A ranar Juma’ar da ta gabata wasu kasashe 30 suka gudanar da taro a Faransa, domin cimma matsaya akan bai hukumar sa ido kan makamai masu guba ikon bayyana bangarorin da ake zargi da amfani da makaman masu guba a dik lokacin da akai zargin amfani da su.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu