Taliban ta yi watsi da tayin kara wa'adin tsagaita wuta
Kungiyar Taliban ta yi watsi da tayin kara wa’adin yarjejeniyar tsagaita wutar da ta sanar tsakaninta da dakarun Afghanistan, domin bai wa ‘yan kasar damar hutun Salla cikin kwanciyar hankali.
Wallafawa ranar:
Cikin sanarwar da ta fitar, kungiyar ta ce, yarjejeniyar da ta ke kai , za ta kare ne a daren yau Lahadi, kuma kai tsaye za ta ci gaba da kai wa sojin gwamnati hare-hare.
A ranar Asabar, shugaban Afghanistan Ashraf Gani ya roki kungiyar ta Taliban, ta bi sawun matakin da ya dauka na tsawaita wa’adin yarjejeniyar tsagaita wutar da suka sanar gabannin ranar Salla, abinda ya baiwa mayakan damar shiga cikin biranen kasar tare da gaisawa cikin raha da sojin kasar da fararen hula cikin raha.
A gefe guda yayin da yarjejeniyar tsagaita wutar ke ci gaba da aiki a ranar Asabar, wani harin kunar bakin wake da aka kai kan wani taron mayakan Taliban da jami’an gwamnati, ya hallaka mutane 36 a lardin Nangarhar, wanda kungiyar IS ta yi kirarin kai wa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu