Yan Sanda sun musanta zargin raunata dalibai a Bangladesh
Dalibai da dama ne suka jikata a Bangladesh a jiya bayan wata bata kashi da yan sanda.Rahotanni daga kasar na nuni cewa yan Sanda sun yi amfani da harsashen roba da ayaki mai sa kwalla wajen tarwatsa masu zanga-zanga.
Wallafawa ranar:
Mai Magana da yahu yan sandan kasar Masudur Rahman ya musanta haka, bayan da wani rahoto ke tabbatar da cewa yan sanda sun raunata dalibai 115.
Haka zalika ministan sufurin kasar Obaidul Quader ya yi watsi da zargin ,inda ya bayyana cewa ana kokarin shafawa yan sandan kasar kashi kaji.
Gwamnatin Firaminista Sheikh Hasina na fuskantar boren jama’a kama daga shekara ta 2009 dangane da tsarin daukar ma’aikata da wasu matsalloli da suka shafi rayuwar al’umat.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu