Afghanistan-Taliban
Taliban ta tsananta kai hare-hare yankin 'yan kabilar Hazaras
Rahotanni Daga kasar Afghanistan sun ce an samu karuwar kai hare hare daga kungiyar Taliban a Yankin da 'yan kabilar Hazaras tsiraru su ke, yayin da Jakadan Majalisar Dinkin Duniya Zalmay Khalizad ya isa yankin domin shawo kan kungiyar ta rungumi zaman lafiya.
Wallafawa ranar:
Talla
Kakakin 'yan Sandan Yankin, Ahmad Khan Sirat ya ce wani fada da ya barke da asubahin jiya a Yankin Ghazni, ya haifar da kashe 'yan Tawaye 15 da sojojin gwamnati 10, yayin da wasu 6 suka jikkata.
Kakakin kungiyar Taliban Zabiullah Mujahid ya bayyana cewa sojojin gwamnati 22 suka kashe.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu