Harin Afghanistan ya kashe mutane 43
Akalla mutane 43 ne suka rasa rayukansu sakamakon harin da wasu ‘yan bindiga suka kai kan wani ginin gwamnati da ke birnin Kabul na kasar Afghanistan a ranar Litinin.
Wallafawa ranar:
Rahotanni sun ce da farko maharan sun tarwatsa wata mota ce da aka shake da bama-bamai, kafin daga bisani su buda wuta a kan ginin ma’aikatar manyan ayyuka da ke birnin na Kabul.
Ma’aikatar Lafiya ta bayyana harin a matsayin daya daga cikin mafi muni da aka kai wa birnin cikin wannan shekara da ke daf da kawo karshe.
Kawo yanzu babu wata kungiyar ‘yan tawaye da ta dauki alhakin kaddamar da farmakin, yayin da mai magana da yawun kungiyar Taliban, Zabiullah Mujahid ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na AFP cewa, ba su da hannu a kazamin harin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu