Isa ga babban shafi
India-pakistan

India ta kai hare-haren jiragen sama kan Pakistan

Kasar India ta ce, ta kaddamar da hare-haren sama akan ‘yan tawayen yankin Kashmir da ke Pakistan, in da ta kashe da dama daga cikinsu.

Hare-haren jiragen saman ya dada sukurkuta dangantaka tsakanin kasashen India da Pakistan
Hare-haren jiragen saman ya dada sukurkuta dangantaka tsakanin kasashen India da Pakistan Reuters/路透社
Talla

Gwamnatin India ta ce, dakarunta sun kai hare-haren ne kan sansanin horar da mayakan Kungiyar Jaish-e-Mohammad da ke Balakot, kuma hakan na zuwa ne wata guda da wani harin kunar bakin wake ya kashe sojojin India 46 a Kashmir.

Ministan Harkokin Wajen India, Vijay Gokhale ya shaida wa manema labarai cewa, daga cikin wadanda hare-haren saman suka hallaka har da kwamandojin ‘yan tawayen.

Matakin kaddamar da harin na baya-bayan nan ya kara nuna yadda kasashen biyu masu makaman nukiliya ke ci gaba da takun saka da juna.

Kaddamar da farmakin na zuwa ne bayan wata majiyar asiri ta ce, Kungiyar Jaish-e-Mohammad na shirin kaddamar da wani sabon harin kunar bakin wake a India.

karon farko kenan tun shekarar 1971 da ake kai harin sama a kan iyakar da ta raba kasashen biyu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.