Kazakhstan ta sauya sunan babban birninta
Majalisar Kasar Kazakhstan ta amince da dokar sauya sunan babban birnin kasar daga Astana zuwa Nursultan domin girmama tsohon shugaban kasa Nursultan Nazarbayev wanda ya sauka daga mukaminsa a jiya Talata bayan kwashe shekaru 30 kan karagar mulki.
Wallafawa ranar:
Shugaban kasa na riko, Kassym-Jomart Tokayev ya gabatar da bukatar sauya sunan ga majalisar, wadda ba tare da bata lokaci ba ta amince da maatakin.
Har ila yau Majalisar Dokokin Kasar ta amince da 'yar tsohon shugaban Dariga a matsayin shugabar Majalisar Dattawa, bayan shugaban majalisar ya zama shugaban kasa na riko.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu