Isa ga babban shafi
Philippines

Iceland ta bukaci hukunta Duterte bisa halaka mutane dubu 27

Yan siyasa da kungiyoyin fararen hula a Philippines, sun goyi bayan kudurin da ya bukaci majalisar dinkin duniya, ta dauki mataki kan gwamnatin shugaban kasar Rodrigo Duterte, bisa dubban mutanen aka kashe da sunan yaki da masu tu’ammuli da miyagun kwayoyi.

Shugaban kasar Philippines Rodrigo Duterte.
Shugaban kasar Philippines Rodrigo Duterte. © Reuters
Talla

Kasar Iceland ce dai ta gabatarwa hukumar kare hakkin dan adam ta majalisar dinkin duniya, bukatar bincikar gwamnatin Duterte, da ake zarginta da halaka mutane akalla dubu 27, bayan kaddamar da yaki miyagun kwayoyi.

Zuwa yanzu kasashe 28 ne suka goyi bayan kudurin, mafi akasarinsu na Turai, inda kuma ake sa ran a ranar 12 ga watan Yuli, manbobin hukumar kare hakkin ta duniya za su kada kuri’a akai.

A shekarar bara kotun duniya ICC ta kaddamar da bincike kan shugaban kasar ta Philippines Rodrigo Duterte dangane da yakar tu’ammuli da miyagun kwayoyi da ya kaddamar a watan Yuli na shekarar 2016.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.