Harin bam ya halaka mutane 62 a Masallaci
Wani harin bam yayi sanadin salwantar rayukan fararen hula 62, tare da jikkata wasu 36, yayinda suke halartar Sallar Juma’a a lardin Nangahar.
Wallafawa ranar:
Hukumomin kasar ta Afghanistan dai sun bada bayanai mabanbanta kan tushen harin, inda gwamnan lardin na Nangahar Ataullah Khogyani ya ce an dasa bama bamai 2 ne cikin masallacin Juma’ar.
Sai dai kakakin shugaban kasar Sadiqi Saddiqi ya ce wani dan kunar bakin wake ne ya tarwatsa kansa a Masallacin.
zuwa lokacin da muka wallafa wannan labarin dai, babu wata kungiya, da ta dauki alhakin kai harin, sai dai kungiyar mayakan Taliban, tayi Allah-wadai da harin, tare da bayyana shi a matsayin ta’addancin kungiyar IS, ko kuma gwamnatin kasarta Afghanistan.
Wani rahoton majalisar dinkin duniya a ranar Alhamis, ya ce hare-haren bam kan wuraren da fararen hula ke taruwa yayi sanadin halakar adadin da ya kai 647 da kuma jikkata wasu dubu 2 da 796, daga watan Janairun 2019 zuwa Oktoba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu