Isa ga babban shafi
Hong Kong

An yanke kunnen wani dan siyasa a Hong Kong

Masu zanga – zanga a Hong Kong sun nuna alamun cewa suna iya fitowa gangami a yau Lahadia manyan shagunan sayar da kayayyakin masarufi, mako daya bayan makamancin gangamin ya rikide zuwa tarzoma tsakaninsu da ‘yan sanda.

Shugabar gwamnatin Hong Kong  Carrie Lam
Shugabar gwamnatin Hong Kong Carrie Lam REUTERS/Umit Bektas
Talla

A karshen makon da ya gabata masu zanga – zangar kin jinin gwamnatin yankin suka yi cincirindo a wani katafaren shago, yayin da wani mutun ya ratsa taron da sharbebiyar wuka, inda har ma ya yanki rabin kunnen wani dan siyasa.

An shirya wasu jerin gangamin a saura biranen yankin, don nuna rashin amincewa da halayyar ‘yan sanda da katsalandar da suke zargin China da yi a harkokin siyasar kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.