An gano mutum daya dauke da cutar SARS a Amurka
Mutane akalla 9 ne suka rasa rayukan su sanadiyyar bular cutar mura a wani yankin kasar ta China.Mutane 400 suka kamu da cutar, kuma kamar yadda hukumomin kasar ke cewa suna daukan matakan dakile ta, ganin yadda take ta yaduwa.
Wallafawa ranar:
Shugaban China a wani sako da aike ga al’uma ya bukaci yan kasar da su dau matakan da suka dace wajen aiki da matakan kariya, jami’an kiwon lafiya a kasar sun mayar da hankali wajen tattance mutanen da suka kamu da wannan kwayar cuta.
Wasu kasashen Duniya sun soma mayar da hankali ga matafiya daga China, a Amurka an gano mutum daya dake dauke da kwayar cutar, lamarin da Hukumar lafiya ta Duniya take shirin gudanar da taro a kai domin duba irin matakan da ya dace kasashen Duniya su dauka don kawo karshen kwayar cutar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu