Asiya
Yan Rohingya 14 suka nitse a ruwa
Akalla yan kabilar Rohingya 14 suka nitse a ruwa yau da safe lokacin da kwale kwalen da suke ciki da yake dauke da mutane da dama ya kife a kudancin kasar Bangladesh.
Wallafawa ranar:
Talla
Kwamandan dakarun dake kula da gabar ruwa, Naim ul Haq ya sanar da cewar sun ceto mutane 70 da ran su, yayin da suka zakulo gawarwaki 14.
Rahotanni sun ce mutane da dama daga cikin yan kabilar Rohingya sama 700,000 da suka samu mafaka a Bangladesh na kokarin barin kasar zuwa Malaysia ta cikin ruwa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu