Isa ga babban shafi
Jamaica

Jam’iyyar adawa a Jamaica ta lashe zabe

Babbar Jam’iyyar adawa a kasar Jamaica, ta People’s National Party, ta lashe zaben kasar da aka gudanar, wanda batun tattalin arzikin kasa ya mamaye yakin neman zabenta.

Masu kokarin kada kuri'arsu a zaben kasar Jamaica
Masu kokarin kada kuri'arsu a zaben kasar Jamaica REUTERS/A. Gilbert Bellamy
Talla

Wannan nasarar da Jam’iyyar ta samu na nuna cewa, shugabanta Portia Simpson Miller, zata koma matsayinta na Fira Minista.

Tuni dai Jam’iyyar Labour mai mulki ta amsa shan kaye a zaben.

Uwar gida Simpson Miller mai shekaru 66, an fara zabenta a Majalisar kasar a shekarar 1976, kuma it ace mace ta farko matsayin Fira minista tsakanin shekarar 2006-2007.

Akwai dai Kalubale babba da ke a gabanta game da bashin da ake biyar kasar tare da matsalar rashin aikin yi da ke addabar ‘yan kasar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.