Cambodia: Mutane uku sun mutu wajen ceto Kare a Rijiya
‘Yan sandan kasar Cambodia sun tabbatar da mutuwar mutane Uku a cikin Rijiya a gabacin kasar a lokacin da suke kokarin ceto rayuwar wani Kare da ya fada a cikin rijiyar. Al’amarin ya faru ne a yankin Kratie a jiya Assabar inda wani Matashi mai suna Say Phalla dan shekaru 25 ya fara fadawa a cikin rijiyar mai zurfin kafa 32 bayan karensa ya fada a ciki.
Wallafawa ranar:
Daga nan ne kuma mahaifiyar shi da wani makwabcinsu suka abka cikin rijiyar domin tsamo Phalla da ya fada a rijiyar don ceto Karen shi.
‘Yan sanda sun yi nasarar tsamo gawawwakin mutanen da kuma gawar Karen daga cikin rijiyar bayan sun samu labarin faruwan al’amarin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu