Isa ga babban shafi
Chile

Za a biya fursunonin siyasa diyya a Chile

Kotun Kolin kasar Chile ta umurci gwamnatin kasar ta biya diyyar sama da Dala miliyan shida da rabi ga mutane 31 da aka tsare su saboda tirsasawar siyasa a karkashin gwamnatin kama-karya ta Augusto Pinochet.

Tsohon Shugaban Chile Augusto Pinochet
Tsohon Shugaban Chile Augusto Pinochet GETTYImages
Talla

Kotun tace ta gamsu da shaidun da aka gabatar ma ta na cin zarafin da aka yi wa fursinonin siyasar lokacin da ake tsare da su a tsibirin Dawson.

Kotun ta yi watsi da bukatar gwamnatin kasar na watsi da karar inda ta bukaci a biya mutanen 31 makudan kudade saboda halin da aka jefa su iyalansu a ciki.

Fursunonin dai sun kunshi jiga-jigan ‘Yan siyasa da Ministoci gwamnatin gurguzu ta Salvador Allende wanda Pinochet ya yi juyin mulki a 1973.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.