Amurka za ta datse tallafinta ga Falasdinawa
Kasar Amurka za ta datse tallafin tattalin arziki da ta ke ba gwamnatin Falasdinawa saboda rikicin masallacin al Aqsa tsakaninsu da Isra’ila, kamar yadda Wata majiyar Diflomasiyar kasar ta bayyana.
Wallafawa ranar:
Rahotanni sun ce Amurka za ta datse tallafin da ta ke ba Gaza da Yamma da Kogin Jordan daga dala Miliyan 370 zuwa dala Miliyan 290.
Sakataren harakokin wajen Amurka John Kerry a ziyarar da ya kai a Amman ya tabbatar da matakin datse tallafin ga Falasdinawa.
Kerry kuma yace Amurka da Isra’ila sun amince da daukar wasu matakai na kawo karshen rikici a masallacin Al Aqsa da ke birnin Kudus inda ake rikici tsakanin Yahudawa da Falasdinawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu