An tabbatar da mutuwar mutane 413 a Ecuador
Gwamnatin Ecuador ta tabbatar da mutuwar mutane 413 sakamakon girgizar kasa da ta afaka wa kasar a karshen mako, yayin da kimanin dubu 2 da 500 suka samu raunuka.
Wallafawa ranar:
Girgizar kasar mai karfin maki 7.8 ta faru ne a ranar Asabar din da ta gabata yayin da jami’an agaji ke ci gaba da aikin ceto.
A lokacin da ya kai ziyara a yankin da ibtila'in ya shafa, shugaban kasar Rafael Correa ya bayyana cewa aikin sake gina inda lamarin ya faru zai lakume biliyoyin dala.
Correa ya ce, wannnn musibar ita ce mafi muni da Ecuador ta gamu da ita a cikin shekaru 70 da suka gabata.
An dai gudanar da jana’izar wasu daga cikin mamatan da girgizar kasar ta kashe a biranen Portoviejo da Pedernales, inda abin ya fi kamari.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu