Isa ga babban shafi
China

An bude taron G20 a Chana

A yau ne aka bude taron shekara na kasashen da suka fi habbakar tattalin arzikin duniya da ake kira G20 a Chana inda shugaban Kasar Xi Jingpin ya bukaci shugabanin kasashen dasu kauce yin alkawarin baki wajen aiwatar da yarjejeniyar da suka kulla.

Shugaban kasar Chana Xi Jinping a yayin jawabin bude taron G20 a birnin Hangzhou, na Chana
Shugaban kasar Chana Xi Jinping a yayin jawabin bude taron G20 a birnin Hangzhou, na Chana Reuters/路透社
Talla

Yayin jawabi a wajen taron da akeyi a kasar China, shugaba Jingpin ya bayyana cewar har yanzu tattalin arzikin duniya na fuskantar mawuyacin hali da suka hada da rashin habbaka kamar yadda ya dace, ga faduwar kasuwanni, da kuma banbancin yarjeniyoyin kasuwancin da kasashen suka kulla.

Shugaban ya bayyana fatar ganin wanan taron ya gabatar da hanyoyin da za’a bunkasa tattalin arzikin duniya da kuma inganta shi kamar yadda yake a baya.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.