Isa ga babban shafi
MDD

Guterres ya zama sakatare janar na MDD

Tsohon Firaministan kasar Portigal Antonio Guterres, na gab da darewa kan mukamin babban magatakarda na Majalisar Dinkin Duniya bayan da a yau kasashe 15 mambobi a kwamitin tsaro na Majalisar sun jefa kuri’a zagaye na shida da ke tabbatar da cewa ya fi sauran ‘yan takara samun kuri’u.

Sabon sakatare janar na Majalisar Dinkin Duniya Antônio Guterres
Sabon sakatare janar na Majalisar Dinkin Duniya Antônio Guterres REUTERS/Denis Balibouse/File photo
Talla

Jim kadan bayan jefa kuri’ar a wannan laraba, jakadan Rasha a Majalisar Dinkin Duniya Vitaly Churkin, ya ce ba wata tantama Guterres ne zai dare kan wannan mukami.

Mr. Guterres mai shekaru 67, shi ne wanda ya jagoranci hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya na tsawon shekaru 10.

A ranar 1 ga watan Janairun badi ne, sabon magatakardan zai fara aiki bayan Ban Ki Moon ya sauka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.